Manyan kungiyoyi na rububin Bellingham



Bellingham

Asalin hoton, OTHER

Rahotanni sun nuna cewa ana takarar tsakanin Liverpool da PSG da Manchester City da kuma Real Madrid kan son saye dan wasan tsakiyar Ingila, Jude Bellingham.

Bellingham na wasa ne a Borrussia Dortmund da ke Jamus, kuma yana da kwantiragi har sai 2025.

Matashin dan wasan na daga cikin wadanda suka haska sosai a gasar kofin duniya da aka kammala a Qatar, kuma ana sa ran duk kungiyar da za ta saye shi daga cikin manyan kungiyoyin, ba zata biya kasa da fam miliyan 100 ba.

Dama Liverpool ta dade tana sa ido kan dan wasan, kuma shigowar Manchester City da kuma darajar gasar Premier League, na nufin akwai yiwuwar Bellingham ya je Ingila.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like