Manyan ‘Yan Siyasa Na Neman Gurgunta Shirin Tallafawa Ta Talakawa Na 5000



Sakamakon wani bincike ya nuna cewa ‘yan siyasa na neman gurgunta Shirin Shugaba Muhammad Buhari na ba talakawa Naira dubu biyar a kowane wata inda suka yi katutu wajen zaben wadanda za su ci ajiyar shirin a jihohin da aka tsara aiwatar da shirin.
An dai tsara aiwatar da shirin ne a jihohin Borno, Kwara  Bauchi, Cross River, Niger, Kogi, Oyo, Ogun da Ekiti sai binciken ya nuna cewa a jihar Kwara inda aka fara biyan kudaden, masu kula da shirin sukan bayar da 5000 ce ga iyalan gida guda sabanin yadda aka tsara ba mutum guda a cikin dangi.

You may also like