Maroko ta kai karar lafarin da ya busa wasanta da Faransa



Morocco

Asalin hoton, Getty Images

Hukumar kwallon kafar Maroko ta sanar da hukumar kwallon kafa ta duniya cewa bata gamsu da bushin lafarin da ya jagoranci wasan da suka yi da Faransa ba ranar Laraba.

An cire Maroko a zagayen kusa da karshe na gasar cin kofin duniya ta Qatar 2022.

FMRF ta ce Lafari Cesar Ramos dan kasar Mexico ya hana su fenareti kafin aje hutun rabin lokaci, a lokacin da Theo Hernandez ya hada jiki da Sofiane Boufal a da’ira ta sha takwas.

A maimakon hakama sai ya bai wa Boufal katin gargadi cewa shi ne ya yi keta.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like