Maroko ta yi wa Najeriya fintinkau a duniya tamaula-Rohr



Rohr

Asalin hoton, OTHER

Tsohon kocin tawagar Super Eagles ta Najeriya Gernot Rohr, ya ce a halin da ake ciki Maroko ta dade da yi wa Najeriya nisa a fagen ci gaban kwallon kafa.

Rohr ya fada wa jaridar Augsburger-Allgemeine cewa, ”rashin kayan wasanni da suka hada da filayen atisaye da karanci koyar da ilimin ita kanta kwallon kafa a Najeriya babban cikas ne gareta dama wasu kasashen Afrika.”

” Mafi yawancin kungiyoyin kwallon kafa a Najeriya basu da matakin kananan yara duk da kasar na da matasa da suka iya kwallo.”

”Makarantun kwallo na yan kasuwa ne kawai ke kokari, kuma suma neman kudi ne ya dame su, na suga cewa sun samar da kwararru,” in ji Rohr.



Source link


Like it? Share with your friends!

-1

You may also like