Maryam Sanda Ta Nemi Kotu Ta Bayar Da Belinta Domin Tana Da Juna Biyu


Matar nan da ta kashe mijinta kwanaki, Maryam Sanda ta roki kotu ta bayar da belinta saboda tana dauke da juna biyu na mijin nata, Marigayin Bilyaminu Mohammed Bello.

Tun a watan Nuwamba ake tsare da Maryam Sanda a gidan kurkukun Suleja bayan da kotu ta ki bayar da belinta sakamakon kashe mijinta wanda dan tsohon Shugaban Jam’iyyar PDP na Kasa, Dakta Bello Haliru ne.

You may also like