Masar ta karyata jita-jitan cewa a kwai sansanin Sojojin kasashen waje a cikin kasar


size_810_16_9_presidente-egito

 

Shugaban kasar Masar ya bayyana cewa babu wata kasa da ta kafa sansanin Soja a cikin kasar

A yayin firarsa da Jaridar Misri, Shugaban Kasar Masar Abdulfatah Alse-se ya karyata jita-jitan cewa a kwai Sansanin Sojan Rasha a arewa maso gabashin kasar sannan ya ce a halin yanzu babu wata kasa daga cikin har da Rasha da ta kafa sansanin Soja a cikin kasar kuma ko nan gaba Gwamnati ba za ta bayar da dama ga wata kasa ta kafa sansanin Sojojinta a cikin kasar ba.

A yayin da yake magana kan alakar kasar da Rasha, Alsese ya ce domin samun daidaito a siyasar kasa da kasa wajibi ne Masar ta kyautata alakar ta da kasar Rasha.

A yayin da yake bayyani kan alakar kasar sa da kasashen Larabawa, Shugaba Alse-se ya kara da cewa Masar gungu ceĀ  a kungiyar kasashen Larabawa kuma ta nada kyakkyawar alaka da dukkanin kasashen Larabawa.


Like it? Share with your friends!

0

You may also like