Mashayin Direba ya kashe mutane 13 a wajen buki a Calabar



BBC

Haɗarin ya afku ne a lokacin wani bukin a Calabar babban birnin jihar Cross Rivers da ke kudu maso kudancin Najeriya, lamarin da ya janyo rasuwar mutane 14 tare raunata wasu mutum 24.

Mai magana da yawun ‘yan sanda a jihar Cross Rivers, SP Irene Ugbo , ya sanar da BBC cewar su na ci gaba da yunƙuri ceto rayukan waɗanda haɗari ya rutsa da su.

Haɗarin ya faru ne a ranar Talata a lokacin bukin wasa da babura da aka gudanar a titin Mary Slessor a Bogobiri, daya daga cikin manyan hanoyoyi da aka tanada na wasan na bana.

Wani ganau ya ce babur din ya ƙwace wa matuƙin da ke gudun wuce sa’a, wanda hakan ya sa ya kutsa cikin ‘yan kallo.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like