Masu Garkuwa Da Mutanen Hanyar Kaduna Zuwa Abuja Sun Shiga Hannu



A garin Jere dake Jahar Kaduna jami’an tsaro sun yi nasarar cafke wasu masu garkuwa da mutane domin neman fansa su 19 wadanda suka addabi hanyar Abuja zuwa kaduna da Kano 

Haka kuma wadanda akayi nasarar chafkewar sun hada da masu sayarda makamai da albarusai na bindigar AK 47 dama kayan damarar sarki da jami’an tsaro 

Andai gabatar da wadannan yan ta’addar ne gaban yan jaridu inda mai hulda da manema labarai na hukumar Yan sandar wato CSP Jimoh Moshood ya jagoranta a garin jeren dake jahar ta kaduna 

Haka kuma hukumar ta jami’an tsaro tayi nasarar kwace wasu bindigogi kirar AK47 guda 8, hadi da wasu bindigogin da dama kirar gida da kuma kayin sarki na jami’an tsaron

Jinjina ga jami’an tsaron Najeriya

Jinjina ga shugaban yan sandar ta kasa wato IGP Ibrahim K. Idris 

Jinjina ga jami’an tsaro na sirri

You may also like