Mata Yan Shi’a Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Neman A Saki Zakzaky 


Bangaren mata na kungiyar yan uwa musulmi da akafi sani da shi’a sun gudanar da zanga-zangar neman a saki shugaban kungiyar Ibrahim El-zakazky wanda ke tsare a hannun jam’ian  tsaro tare da mai dakinsa. 

Zanga-zangar  ta gudana ne a ofishin hukumar kare Hakkin Dan Adam Ta Kasa.

Masu zanga-zangar sun zargi gwamnati da kin bin umarnin hukuncin da kotuna suka yanke na a saki shugaban kungiyar.

Sai dai gwamnatin tace tana cigaba da tsare shugaban kungiyar ta shi’a ne  domin tsaron lafiyarsa.

Kungiyoyin kare hakkin bil-adama da dama sun sha kiraye-kirayen gwamnati  ta sake shi amma tayi kunnen uwar shegu da kiran nasu. 

Abin jira a gani shine ko yaushe shugaban kungiyar ta yan uwa musulmi zai shaki iskar yanci.   


Like it? Share with your friends!

0

You may also like