Wata kungiyar matasan masarautar Daura mai suna Daura Emirate Youth Progressive Movement (DEYPM) ta yi alkawarin sayawa shugaban kasa Muhammad Buhari fam ɗin tsayawa takara a shekarar 2019.
Kungiyar ta kuma ce zata sayawa gwamna Aminu Bello Masari fom na tsayawa takara a shekarar 2019.
Abdulkadir Lawal, shugaban kungiyar shine ya bayyana haka yayin wani taron gangami da aka gudanar a Katsina.
Taran gangamin ya samu halartar dubban matasa da suka fito daga kananan hukumomi biyar dake ƙarƙashin masarautar Daura.
“Zamu sai musu fom ɗin a matsayin gudunmawarmu na goyon bayan jagororin siyasar biyu kan su sake tsayawa takara a karo na biyu a zabe,” ya ce.
Ya ce kungiyar ta yanke shawarar sayawa Buhari da Masari fom saboda kwazon da suka nuna.
Lawal yace Shugabannin biyu sun kawo cigaba cikin sauri a wuraren da suke jagoranci musamman bangaren tsaro, aikin noma da sauransu.
“Gwamna Masari ya samu nasara wajen bunkasa ilimi, kiwon lafiya abubuwan more rayuwa a jihar cikin shekara biyu da yayi,”