Matsalolin da aka fuskanta lokacin zaɓen gwamna a wasu jihohin Najeriya



BBC
Bayanan hoto,

An riƙa fuskantar tashin-tashina a wasu jihohi wanda fafatawar ta yi zafi a cikinsu.

Tashin hankali da rikici da barazana ga masu zaɓe na daga cikin abubuwan da suka mamaye zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar jihohi da aka yi a jihohi 28 cikin 36 da Najeriya ke da su a ranar 18 ga watan Maris na 2023.

Tun da fari an tsara gudanar da zaɓen a ranar 11 ga watan Maris amma an sauya hakan bayan ƙarar da jam’iyyun adawa suka shigar na ƙalubalantar zaɓen shugaban ƙasa da ya gudana a ranar 25 ga watan Fabrairu.

An fara zaɓen kan lokaci a wasu sassan ƙasar, ba kamar yadda aka yi ba a zaɓen shugaban ƙasa da ba a fara zaɓen ba ma a wasu sassan har sai da lokacin da aka tsara farawar ya wuce.

Rikici da hana masu zaɓe fitowa

A Kano, inda nan ne cibiyar kasuwanci ta arewacin Najeriya, wani wakilin BBC ya shaida yadda ‘yan daba suka rika kai hare-hare rumfunan zaɓe.



Source link


Like it? Share with your friends!

1

You may also like