Mayaƙan Boko Haram Sun Kashe Ma’aikatan Jin Kai Su Hudu a Rann


Kamfanin Dillancin Labaru Na Nijeriya ya tabbatar da cewa mayakan Boko Haram sun kashe ma’aikatan Jin kai na kasa da kasa a yayin wani mummunan hari da suka kai garin Rann da ke karamar hukumar Kala Balge a jihar Borno.

Rahotanni sun nuna cewa mayakan Boko haram din sun kai harin ne a jiya Alhamis da misalin Karfe bakwai na Yamma inda suka arce da wata Ma’aikaciyar jinya guda daya. Daga cikin ma’aikatan jinya da suka kashe har da likita guda.

You may also like