MDD ta gargadi Sudan ta Kudu kan sabon Yaki


 

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadi a game da sake barkewar kazamin fada a kasar Sudan ta kudu, bayan Gwamnatin kasar ta yi watsi da  jita-jitar da ke ta yawo a kasar cewa shugaban kasar Salva Kiir ya mutu.

Majalisar ta ce abin damuwa ne yadda ake ci gaba da samun hargitsi a sassan kasar, da fargaban kar lamarin ya kazance.

Jami’an Majalisar sun kuma koka da yadda ake hana su kai ga wasu wurare da ake rikici a kasar.

Tun ajiya ne dai Ministan Labaran kasar, Michael Makuei, ya fadawa manema labarai cewa shugaba Salva Kiir na nan tangaran, bai mutu ba kamar yadda wasu ke yada wa.

You may also like