Mece ce gwamnatin riƙon-ƙwarya da ‘wasu ke son kafawa’ a Najeriya?



...

Asalin hoton, Getty Images

A ranar Laraba ne hukumar ƴan sandan ciki ta Najeriya ta tabbatar da raɗe-raɗin da ake yi cewar akwai wata ƙullaliya ta ganin an kafa gwamnatin riƙon-ƙwarya a ƙasar.

Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar ta DSS, Peter Afunaya ya sanya wa hannu ta ce “wani yunƙuri ne na jingine kundin tsarin mulki da yin zagon ƙasa ga mulkin farar hula da kuma yunƙurin jefa ƙasar cikin ruɗani.”

Sanarwar ta ƙara da cewa “masu kitsa lamarin sun tattauna kan hanyoyi da dama na aiwatar da shirin nasu, kamar haddasa mummunar zanga-zanga a manyan biranen Najeriya, wadda za ta haifar da ƙaƙaba dokar-ta-ɓaci.”

“Ko kuma ta hanyar nemo izinin kotu domin dakatar da rantsar da sabuwar gwamnati da majalisar dokokin tarayya, ta hanyar da ba ta dace ba.”



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like