Mendy na neman City ta biya shi miliyoyin kudi



Benjamin Mendy

Asalin hoton, Getty Images

Benjamin Mendy zai kai tsohuwar kungiyarsa Manchester City kara, domin a biya shi miliyoyin kudi, bayan ta daina biyan sa albashi.

Dan kwallon tawagar Faransa, mai shekara 29 ya bar Etihad ne a karshen kakar da kwantiraginsa ya kare, kafin fara wasannin bana.

An wanke shi da soso da sabulu kan zargin fyade da tuhume-tuhumen da suka shafi fyade da aka yi masa.

An ce City ta daina biyan Mendy albashi tun daga Satumban 2021, bayan da aka tuhume shi, sannan aka tsare shi.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like