Ministan Cikin Gidan Kasar Tunisiya ya tsalle rikiya da baya


 

 

Majiyar tsaron kasar ta Tunsiya tana cewa; Hadi Majzoon ya tsallake rijiya ta baya a wani harin ta’addanci.

Majiyar tsaron kasar ta Tunsiya tana cewa; Hadi Majzoon ya tsallake rijiya ta baya a wani harin ta’addanci.

Jaridar “al-Shoroq’ ta kasar Tunisiyan  ta buga cewa; Rundunar musamman wacce ta ke fada da ayyukan ta’addanci ta dakile wani shirin ta’addanci na hallaka ministan harkokin cikin gidan kasar Hadi Majazoob.

Rundunar ta sanar da cewa; “Yan ta’addar sun so kai wa ministan harkokin cikin gidan hari a yayin da ya ke kan hanyarsa ta zuwa gidan mahaifinsa.

Tuni an mika mutanan ne dai ga alkali domin ya gudanar da bincike.

You may also like