Mugabe Ya Sanar Da Fara Kamfen Don Tsayawa Takakar Zaben 2018



Shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe mai shekaru 93 wanda kuma ya dauki tsawon shekaru 37 yana shugabancin kasarsa ya bayyana cewa, ya fara yakin neman zabe domin tsaya wa takara a zaben shugaban kasar da za a yi a shekarar 2018.

Labaran da jaridun kasar suka fitar na cewa, Mugabe ya yi jawabi a ofishin jam’iyyar Zanu PF a Harare babban birnin kasar inda ya ce, ya fara kamfe din sake tsaya wa takara a zaben daza a yi a shekara mai zuwa.

Ya ce, gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki don ganin ‘yan asalin Afirka kuma bakaken fata sun fi mallakar kasa a Zimbabwe.

Mugabe ne shugaban kasa a nahiyar Afirka da ya fi kowanne tsufa. 

Ya kuma ce, baya ga shi bai ga wani dan takara da ya dace da kasarsa ba.

You may also like