Muhimman abubuwan da suka faru a Najeriya a 2022



mahara a kan babura

Janairu – Shekarar 2022 ta fara bude shafinta a arewacin Najeriya da hare-hare inda tun daga ranar 4 zuwa 6 ga watan Janairun sabuwar shekarar ‘yan bindiga haye a babura kimanin 300 suka kai hari wasu garuruwa guda biyu na Kurfar Danya da Rafin-Gero a kananan hukumomin Anka da Bukkuyum.

Sun kashe mutum kimanin 200, bayan bude wuta irin ta kan mai uwa da wabi tare da kona gidaje da abinci da dabbobi.

Janairu – Da yammacin ranar 14 ga watan Janairu ne dai har wayau ‘yan bindiga suka kashe mutum akalla 50 a kauyen DanKade da ke jihar Kebbi, bayan sun kone rumbunan garin sannan sun yi artabu da jami’an tsaro inda suka kashe dan sanda da soja.

Fabrairu –  A watan Fabrairu ne kungiyar malaman jami’a ta ASUU ta tsunduma cikin yajin aikin bisa neman martaba wasu jerin yarjejeniyoyi da ta yi da gwamnatin tarayya a shekarun baya.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like