Muna fama da ƙarancin kuɗi – Gwamnatin Kenya



Shugaban Kenya, William Ruto

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,

Shugaban Kenya, William Ruto

Gwamnatin Kenya ta fito ta amince kan cewa kasar na fama da ƙarancin kuɗi wanda hakan ya sanya aka samu jinkiri wajen biyan albashin ma’aikatan gwamnati.

Gwamnatin ta ce dole ne ta sanya ta ɗaukan matsaya, tsakanin biyan albashi ko kuma ci gaba da biyan bashin kasashen waje da ake bin ta.

Jami’ai a ma’aikatu da hukumomin gwamnati ne jinkirin biyan albashin ya fi shafa.

Ministan kuɗin ƙasar, Njuguna Ndung’u ya ce gwamnati na fuskantar matsalolin kuɗi saboda ƙarancin haraji da kuma gaza samun bashi.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like