Mutane 27 sun mutu sakamakon fashewar kayan wasan wuta a kasar Mekziko


 

 

Mutane 27 ne suka mutu sakamakon hatsarin da ya afku a kasuwar sayar da kayan wasan wuta a kasar Mekziko.

Rahotanni sun ce, lamarain ya afku a kasuwar da ake sayar da kayayyakin na wasan wuta domin bukukuwan sabuwar shekara.

Sama da mutane 70 ne  suka jikkata sakamakon lamarin wanda ya afku a yankin arewa da garin Mekziko da nisan kilomita 20.

A wannan kasuwa dai a shekarun 2005 da 2006 an samu afkuwar lamari makamancin wannan.

You may also like