Mutum 21 aka kashe a tashin hankalin bayan zaɓen gwamnonin Najeriya – EU



EU

Asalin hoton, EU in Nigeria/Twitter

Tawagar Ƙungiyar Tarayyar Turai da ta sa ido a zaɓen gwamnoni da na ƴan majalisar jihohi na ranar 18 ga watan Maris ta ce an kashe kimanin mutum 21 sakamakon tashin hankalin da aka samu a wasu jihohin Najeriya.

EU ta bayyana haka ne yayin da ake ci gaba da sanar da sakamakon zaɓen gwamnoni da na ƴan majalisar dokokin wasu jihohin.

Babban jami’in da ya sanya ido a zaɓen na Najeriya, Mista Barry Andrews ne ya bayyana wa ƴan jarida hakan ranar Litinin game da sakamakon bincikensu da suka yi game da zaɓen.

Barry ya ƙara da cewa mutane da dama ba su fita kaɗa ƙuri’a ba galibi a cewarsa saboda rashin biyan buƙatun masu zaɓe a zaɓen shugaban ƙasar da ya gudana.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like