Najeriya: Ba a biyanmu kuɗin alawus — Masu tsaron iyaka



Jami'an tsaro

Asalin hoton, OTHER

Jami’an tsaron da ke aiki na musamman na kulawa da iyakokin Najeriya da makwabtanta, domin hana satar shigar da kayan da gwamnati ta haramta, sun koka da rashin biyansu alawus-alawus na aikin.

Ma’aikatan sun koka ne tare da yin kira ga wadanda lamarin ya shafa a kan su taimaka a biya su hakkokinsu.

Daya daga cikin ma’aikatan da BBC ta tattauna da shi da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce, suna wahala kwarai da gaske a aikin.

Mutumin ya ce, ma’aikatan da ke aiki a iyakokin Najeriyar don sanya idanu da kuma hana shigar da kayan da aka haramta, sun hadar da sojoji da jami’an hukumar hana fasa kauri da na hukumar shige da fice da kuma na hukumar ‘yan sandan ciki wato DSS.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like