NDLEA ta gano gonakin tabar wiwi uku a jihar Katsina



Jami'an NDLEA

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,

Hukumar ta ce ana fakewa da noman kayan lambu a gonakin na wiwi

Hukumar da ke yaki da miyagun kwayoyi a Najeriya NDLEA ta ce ta gano gonaki uku da ake shuka ganyen wiwi a jihar Katsina.

Mataimakin shugaban hukumar mai kula da harkokin gudanarwa a jihar, Halilu Hamidu ya ce sun samu nasarar gano gonakin ne bayan samun bayanai daga wasu mutane.

Hamidu ya ce wannan shi ne karon farko da hukumar ta gano irin wannan gonar a kauyen Sobashi na karamar hukumar Dutsi.

“Masu gonar suna amfani da ita wajen shuka tabar ta wiwi amma suna fakewa da noman kayan lambu irinsu tattasai da tumatur,” in ji shi.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like