Nijar ta ɗau aniyar sanin duk waɗanda suka mallaki bindigogi a faɗin ƙasar



Makamai

Hukumomi a jamhuriyar Nijar sun ce ‘yan ƙasar sun fara amsa kira, wajen kai bindigoginsu don yin rijista a ƙarƙashin wani shiri da aka ƙaddamar ranar Talata.

Shirin zai tabbatar da yin rijista ga ɗaukacin bindigogin da fararen hula suka mallaka ta hanyar ofishin ministan cikin gida da haɗin gwiwar hukumar yan sanda.

Muhukunta sun ce maƙasudin aikin shi ne yi wa bindigogin lamba don sanin taƙamaiman adadin kayan harbin da ke hannun ‘yan ƙasar, da kuma tantance masu riƙe da bindigogi da izinin gwamnati a illahirin Nijar.

Ba su dai bayyana tsawon lokacin da za a kwashe ana aikin yi wa bindigogin lamba tare da tantance masu riƙe da su da izinin hukumomin ƙasar ba.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like