Pelé a Afirka : Gwanintarsa da tarihi da maganganun da ake lakaba masa



Pele a Kenya

Asalin hoton, Alamy

Bayanan hoto,

Pelé ya ziyarci kasar Kenya a shekarun 1970

Kasancewarsa daya daga cikin manyan taurarin matasan bakaken fata a fagen wasanni a zamanin talabijin, Pelé ya samu karbuwa da kauna daga ‘yan Afirka a fadin nahiyar.

A lokacin da kasashen Afirka ke fafutukar samun ‘yancin- kai a karshe-karshen shekarun 1950 da kuma farko-farkon 1960, Pelé ya rika samun gayyata daga kasashen Afirka da suka samu ‘yanci, domin wasan sada zumunta da kungiyarsa Santos FC da kuma tawagar kasarsa ta Brazil.

A tarihinsa da ya rubuta, Pelé ya bayyana cewa wadannan tafiye-tafiye da ya rinka yi zuwa kasashen Afirka a wannan lokaci ba kawai sun sauya yadda yake kallon duniya ba har ma da yadda ya ce duniya ta dauke shi.

Mutumin da ya rubuta kundin kungiyar kwallon kafa ta Santos, Guilherme Nascimento, ya yi daidai kamar yadda ya nuna cewa wadannan tafiye-tafiye zuwa Afirka na cike da labarai wadanda kusan da wuya a iya bambancewa tsakanin na gaskiya da kuma na kunne-ya-girmi-kaka.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like