Qatar 2022: An kashe wani yaro a Faransa



.

Asalin hoton, AFP

Wani yaro dan shekara 14 ya rasa ransa bayan da mota tabi ta kansa a birnin Montpellier da ke kudancin Faransa.

Lamarin ya faru ne jim kadan bayan kammala wasan kusa da karshe da Faransa ta yi nasara kan Maroko.

Hukumomi sun ce wata mota ce manne da tutocin Faransa a jikinta, tazo a guje ta bi ta kan yaron, kuma ya mutu ne a asibiti.

Yanzu haka yan sanda na kan neman direban motar.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like