Qatar 2022: Wane ne Marciniak, lafarin da zai busa wasan karshe



.

Asalin hoton, OTHER

Kwamitin da ke jagorancin alkalan hukumar kwallon kafa ta duniya, ya zabi Szymon Marciniak a matsayin lafarin da zai busa wasan karshe tsakanin Faransa da Argentina.

Dan kasar Poland din mai shekaru 41, na cikin tawagar alkalan da suka jagorancin wasannin kasashen biyu kafin a kawo wannan mataki na wasan karshe.

Akwai wasan da Argentina ta doke Australia a zagayen kwaf daya, da kuma wanda Faransa ta doke Denmark a wasan rukuni.

Jiya Alhamis ne FIFA ta sanar da sunansa a matsayin wanda zai raba gardama, a wasan da duniya ke dakon gani tuntuni.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like