Rahoto: Shin Gwamnonin PDP Sun Juyawa ATIKU Baya Ne



Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar ya musanta rahotannin cewa ya samu baraka da gwamnonin PDP da kuma Shugaban jam’iyyar na Kasa, Uche Secondus.

A cikin wani jawabi da ya rabawa kafafen Yada Labarai, Tsohon Shugaban ya bayyana wadannan rahotannin a matsayin marasa tushe inda ya nuna cewa an kirkiri labarin ne don a janyo rudani tsakaninsa da gwamnoni. Ya kuma tabbatar da cewa akwai kyakkyawar alaka tsakaninsa da shugabannin PDP.

You may also like