Rayuwar ‘yan cirani na cikin hadari a tekun Bahar Rum | Labarai | DW



Jami’an da ke aikin tsaron gabar ruwan kasar Italiya na gudanar da wani gagarumin aikin ceto rayukan ‘yan cirani da ke cikin wasu jiragen ruwa da aka gano na fuskantar barazanar nutsewa a cikin tekun Bahar Rum. Mutum akalla dubu daya da dari biyu aka kiyasta na cikin jiragen da suka taso daga arewacin Libiya a kan hanyar shiga Turai.

Wata kungiyar mai zaman kanta ta kasar Jamus mai suna Sea-Watch International, wacce ta gano jiragen da taimakon fasahar zamani ta ce, an tura wa jiragen man fetur da ruwa, amma mahukuntan kasar Malta na kawo musu cikas a kokarin ceto mutanen. Kafin aukuwar lamarin na wannan Litinin, rahotanni na cewa, ‘yan cirani kimanin dubu biyu aka ceto daga gabar ruwan Italiyan tun daga ranar Jumma’ar da ta gabata.





Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like