Shugaba Muhammad Buhari ya tabbatar da cewa rasa rayuka da aka yi sakamakon rikicin Fulani da manoma a kwanan nan ya yi matukar girgiza gwamnatin APC.
Shugaban ya ce rikicin ya janyo bakin ciki da kunci ga wasu ‘yan Nijeriya inda ya bayar da tabbacin cewa nan bada jimawa ba, jami’an tsaro za su shawo kan al’amarin.