Rundunar sojin Najeriya za ta kafa sansani a jihar Sokoto


 

Rundunar sojin Najeriya za ta kasa sabon sansanin sojin runduna ta 8 a jihar Sokoto da ke arewa maso-yammacin kasar.

Shugaban rundunar sojin kasa ta Najeriya Laftanal Janar Yusuf buratai ya sanar da cewa, manufar kafa sansanin ita ce, sake samar da tsaro a kan iyaka Najeriya da kasashen waje.

Buratai ya ce, majalisar al’amuran soji ta Najeriya ta amince da a kafa sansanin na runduna ta 8 a Sokoto, kuma za a aike da dakaru daga yankin arewa maso-gabas zuwa sansanin.

Ya ce, da zarar an gama samar da tsaro a yankin arewa maso-gabas to za a tura sojojin zuwa sansanin na Sokoto.


Like it? Share with your friends!

0

You may also like