Rundunar ‘yansandan jihar Kano tayi holen wasu ‘yan fashi da makami da suke addabar al‘umma da sace sace a ciki da wajen jihar.
Kakakin rundunar ‘yansandan jihar kano, DSP Magaji Musa Majiya ya kira ya bayyana musu cewa a cikin yan fashin sun hadar da masu kwacen motoci, kuma daga cikin su akwai wadanda suka je gidan wata mata suka yi mata fashi sannan suka yi mata fyade.