Salah na fatan Liverpool za ta koma ganiya bayan cin Everton



Salah Klopp

Asalin hoton, Getty Images

Mohamed Salah na fatan Liverpool za ta koma kan ganiya, bayan doke Everton 2-0 a wasan mako na 23 a Premier League a Anfield ranar Litinin.

A wasan na hamayya na Mersyside Derby, Liverpool ta fara cin kwallo ta hannun Salah a minti na 36 da fara tamaula.

Sabon dan kwallon da ta dauka a Janairu, Cody Gakpo ne ya ci na biyu na farko da ya zura a raga a Liverpool.

Haka kuma kwallon farko da Salah ya ci a Premier League tun bayan 26 ga Disambar 2023, lokacin da ya ci Aston Villa.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like