Sanusi ya nemi Miyetti Allah da ta tona fulani masu kisa dake cikin ƙungiyar


Sarkin Kano Muhammad Sunusi II, ya nemi ƙungiyar fulani ta Miyetti Allah da ta tona asirin ɓatagarin fulani makiyaya dake cikinta.

Da yake magana a taron shugabannin ƙungiyar na ƙasa da aka gudanar a Minna, jihar Niger  a ranar Lahadi Sunusi yace ba dukkanin fulani bane ɓata gari.

Sarkin ya ce  ƴan Najeriya su daina kawo zancen ƙabila duk lokacin da aka aikata wani laifi.

“Ya kamata ƴan Najeriya su kaucewa alaƙanta wata ƙabila  duk sanda aka aikata wani laifi, laifi  bashi da tambarin wata ƙabila,” yace.

“Ya kamata Miyetti Allah ta haɗa kai da Gwamnonin Niger, Kogi, Nassarawa da kuma Kano wadanda suka nuna sha’awarsu ta bada filayen kiwo domin a samu  inganatasu.”

Ana sa ɓangaren shugaban shiya na ƙungiyar, Gidado Siddiki ya ce maganin rikicin fulani da makiyaya shi ne tattaunawa tsakanin masu ruwa da tsaki a harkar.

Ya yabawa hanyar da gwamna Willie Obiano  na jihar Anambra da kuma  Ifeanyi Ugwuanyi na jihar Enugu suka bi wajen maganin rikicin fulani da manoma.

You may also like