SARAKI YA KALUBALACI BUHARI KAN SAMARWA MATASA AIKIN YI



Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, ya bayyana cewa lokaci ya yi da gwamnatin Buhari za ta mayar da hankali wajen samarwa matasa aikin yi a maimakon zargin gwamnatocin da suka shude kan tabarbarewar tattalin arzikin kasar nan.

Ya kara da cewa babban abin da ke kara yawan rashin aiki a tsakanin matasa shi ne, yawan haihuwa wanda kuma ya zarce ci gaban tattalin arziki sannan kuma tsarin koyar a Makarantu bai tanadi koyar da sana’o’in dogaro da kai ba sai kuma durkushewar masana’antu.

You may also like