Sarkin Morocco Ya Kori Ministoci 12 Daga Cikin Majalisar Ministocin Kasar


 

Sarkin kasar Morocco Muhammad na 6 ya kori wasu daga cikin ministocin gwamnatin rikon kwarya ta kasar.

Tashar talabijin ta Russia Today ta bayar da rahoton cewa, a daren jiya ne sarkin ya sanya hannu kan takardar tsige ministocin guda 12, wadanda dukkaninsu suna daga cikin ‘yan majalisar dokokin da suka lashe zabe da aka gudanar a kasar a ranar 7 ga wannan wata na Oktoba.

Bisa ga dokokin kundin tsarin mu8lkin Morocco, mutum daya ba ya rike mukamin minista alhali yana a matsayin dan majalisa.

Bayan gudanar da zaben na Morocco majalisar ministocin ta yi murabus, amma sarkin ya sake nada domin ci gaba da gudanar da ayyuka na wucin gadi.

You may also like