Saudiyya ta gayyaci shugaban ƙasar Iran zuwa Riyadh



Shuagaban ƙasar Iran

Asalin hoton, Reuters

Iran ta ce Saduiyya ta gayyaci shugaban ƙasar Ebrahim Raisi domin zuwa wata ziyara a ƙasar – mako ɗaya tun bayan da ƙasashen biyu suka amince su ci gaba da hulɗar diflomasiyya.

An bayyana cewa batun gayyatar na kunshe ne cikin wata wasika da Sarki Salman ya rubuta, sai dai ƴan ƙasar basu tabbatar da hakan ba.

Ƙasashen biyu da ke yankin gabas ta tsakiya, sun yi ta samun takun-tsaka na tsawon shekaru.

China tana cikin ƙasashen da suka shiga tsakani wajen ganin ƙasashen sun dawo ɗasawa, abu kuma da aka bayyana cewa zai sauya siyasar yankin.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like