Sayar da katunanku na zaɓe zai cutar da Arewa – Ƙungiyar Dattijai ta NEF



.

Asalin hoton, Getty Images

Ƙungiyar dattijan arewacin Najeriya ta Northern Elders Forum ta nuna damuwa game da zargin cewa wasu ƴan siyasa sun duƙufa wajen sayen katunan zaɓe daga hannun jama’ar yankin.

Ƙungiyar ta ce sayar da katin zaɓen yana da hatsari sosai, saboda zai iya cutar da yankin.

Dr Hakeem Baba Ahmed shi ne kakakin ƙungiyar kuma ya shaida wa BBC cewa sun daɗe da samun labarin yadda ake zagayawa ana karɓar katunan zaɓen jama’a musamman mata.

Ya ce masu yin wannan abu na bijiro da wata dabara ta shawo kan mutane su ba da katinsu da sunan taimaka musu wajen shiga wani shirin yaƙi da talauci.

“Arewa ita ta fi yawan masu rajistar zaɓe, tun fil azal, musamman ma wannan zaɓen da mutane da yawa ke ta rububin ganin sun kaɗa ƙuri’a,”



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like