Seyi Makinde ya lashe zaɓen gwamna a jihar Oyo



Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya, INEC ta ayyana Seyi Makinde na Jam’iyyar PDP a matsayin ɗan takarar da ya lashe zaɓen gwamna a jihar Oyo a zaɓen ranar Asabar da aka gudanar.

Makinde wanda shi ne gwamna mai ci a jihar ta Oyo ya samu ƙuri’u mafi yawa inda ya bai wa babban ɗan adawa a jihar, Teslim Folarin na Jam’iyyar APC tazarar ƙuri’u dubu 300.

INEC ta ce Seyi Makinde ya samu ƙuri’u 563,756 yayin da Teslim Folarin na APC ya samu ƙuri’u 256,685.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like