Shell zai biya manoma a Neja Delta diyyar dala miliyan 16



Shell

Asalin hoton, Getty Images

Kamfanin haƙar ɗanyen man fetur na Shell zai biya diyyar dala miliyan 16 ga wasu manoma a yankin Neja-Delta a kudancin Najeriya.

Hakan na cikin diyyar da kamfani zai biya ga waɗanda malalar man fetur ta yi musu barna a gonakinsu.

Alƙawarin biyan diyyar na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kamfanin ya fitar a ranar Juma’a tare da haɗin gwiwar reshen cibiyar Friends of the Earth a ƙasar Netherlands.

Matakin ya biyo bayan hukuncin kotun Netherlands inda ta kama reshen kamfanin na Shell a Najeriya da laifin malalar mai a shekarar da ta wuce kuma ta umarci Shell ya biya diyya.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like