Shin Magu Zai Bar EFCC Bisa Zaman Sa Kwamishinan Ƴan Sanda?


An fara hasashen cewa Shugaban Hukumar EFCC, Ibrahim Magu zai bar hukumar bisa karin girman da aka yi masa kwanan nan inda ya zama cikakken Kwamishinan ‘yan sanda.

A bisa ka’idar aiki, dole Magu ya tafi kwas a cibiyar horas da manyan jami’an gwamnati da ke Kuru a jihar Filato a matsayinsa na Kwamishinan ‘yan sanda. Wasu na ganin wannan zai inganta dangantaka tsakanin bangaren gwamnati da na majalisa idan har Magu ya koma Makaranta.

You may also like