Shuga Buhari Ya aikewa Da majallisa Takarda Kan Cewa Su Amince Da Nadin Magu



Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rubuta wa majalisar dattijai takarda wadda a cikinta yake bukatar sanatocin su amince da nadin mukaddashin shugaban hukumar yaki da masu yi wa tattalin arziki zagon-kasa; Ibrahim Magu.
Wasikar Buharin dai ta zama martani ga kin amincewar da majalisar dattijan ta yi da nadin Magu a matsayin cikakken shugaban hukumar EFCC, bisa rahoton hukumar tsaro ta kasa.

You may also like