Shugaba Buhari Ya Gana Da Shugabar Kasar Jamus


A safiyar yau, Shugaba Muhammadu Buhari da tawagar Nigeria suka gana da Shugabar Gwamnatin Jamus, Angela Merkel, a Chancellery a birnin Berlin.

Shugaba Buhari a shafinsa na Twitter ya bayyana cewa ganawar na da matukar muhimmanci kuma ta fi maida hankali ne kan tsaro, tattalin arziki da karfafa dangantaka tsakanin Nigeria da Jamus.

You may also like