SHUGABA BUHARI YA KAI ZIYAR FADAR SARKIN KANO



Mai girma shugaban kasa Muhammadu Buhari Tare da Mai Girma Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje da tawagar gwamnatin, yanzu kenan ida suka ziyarci fadar Mai Martaba Sarkin Kano Malam Muhammad Sanusi ll a matsayin sa na Uban Gari.

A yanzu haka kuma shugaban kasa ya kammala jawabin sa ya tabo tarihin gwagwarmayar sa musamman a bangaran harkar siyasa da yadda aka sha wahala.

Ku biyo mu domin yadda zata kaya a ci gaba da ziyarce ziyarcen da PMB ya kawo a jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje.

You may also like