Sojoji sun kashe wasu batagari biyu a Kaduna


Sojojin Najeriya dake aikin Atisayen  AYEM AKPATUMA ya yin da suke gudanar da sintiri akan titin Dogon Dawa -Damari a jihar Kaduna  sun kashe wasu mutane biyu da ake zargin bata gari ne tare da gano bindigogi kirar Ak-47 guda biyu.

Sojojin sun kuma gano gidan harsashi guda uku da kuma harsashi 88 daga bata garin.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar sojin, Birgediya Janar Texas Chuku, ya bayyana cewa a wani bangaren sojoji da aka ajiye akan titi Rigasa zuwa filin jirgi sun fuskanci harin kwanton bauna daga wasu mutane da ba a san ko su waye ba.

Ya kara da cewa sojoji biyu sun jikkata a harin kuma a yanzu haka suna karbar magani a asibiti.

You may also like