Takaddama ta barke tsakanin PDP da APC kan filin taro a Katsina



.

Asalin hoton, PDP

Cacar baki ta kaure tsakanin jam’iyyar APC mai mulki da ta PDP mai hamayya a jihar Katsina da ke arewacin Najeriya.

Lamarin ya faru ne bayan da jam’iyyar PDP ta yi zargin cewa gwamnatin Katsina ta hana ta amfani da filin wasa na Muhammad Dikko da za ta yi gangamin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasarta da na gwamnan jihar da sauran ‘yan takara.

Shugaban kwamitin yakin neman zaben na dan takarar shugabancin Najeriya na PDP a Katsina, Sanata Ibrahim Tsauri, ya ce sun shirya gudanar da taron dan takararsu na PDP, Atiku Abubakar da na gwamnan jihar Sanata Yakubu Lado Dan marke da na sauran ‘yan takararsu a ranar 20 ga Disambar nan a filin kwallon.

Sanata Tsauri ya yi zargin cewar gwamnatin Jihar ta Katsina ta hana su yin amfani da filin tana mai ikirarin cewa ana gudanar da gyara a cikinsa.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like