Taliban ta hana mata aiki a karkashin Majalisar Dinkin Duniya



Mata a Afghanistan

Asalin hoton, Getty Images

Kakakin majalisar dinkin duniya Stéphane Dujarric, ya ce matakin na hana mata da ke aiki da hukumomin majalisar shi ne abun damuwa na baya-bayan nan da ke yi wa hukumomin agaji tarnakin aiki a kasar wadda sama da yawan al’ummarta miliyan 40 ke bukatar taimako.

Ya ce Majalisar na kokarin kaiwa ga mutane miliyan 23 – maza da mata da kananan yara domin ba su agajin da suke matukar bukata su rayu.

Jami’in ya ce suna sa ran tattaunawa da masu mulkin na Afghanistan ‘yan Taliban domin samun cikakken bayani kan hana matan aiki.

Ya ce za su yi kokarin ci gaba da amfani da duk hanyoyin da suka kamata domin tabbatar da ganin sun kai taimakon ga wadanda suke cikin tsananin bukata musamman mata da ‘yan mata da yara.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like