Tashin Bom A Birnin Mogadisho Na Kasar Somaliya Ya Lashe Rayukan Mutane Masu Yawa


 

Majiyar rundunar ‘yan sanda a Somaliya ta sanar da cewa: Tashin wani bom a birnin Magadisho fadar mulkin kasar ya lashe rayukan mutane masu yawa.

Kamfanin dillancin labaran Reuters ya nakalto daga majiyar rundunar ‘yan sandan Somaliya cewa: Wata mota da aka makare da bama-bamai ta tarwatse a kusa da wani ginin otel a birnin Magadisho fadar mulkin kasar a safiyar yau Laraba, lamarin da ya janyo mutuwar mutane akalla 12 tare da jikkatan wasu kimanin 25 na daban.

Rahotonni sun bayyana cewa: A bayan tashin bom din wasu gungun ‘yan bindiga sun kutsa cikin otel din da nufin yin garkuwa da mutane, amma har yanzu babu cikakken bayani kan halin da ake ciki.

You may also like