‘Tinubu bai gana da alƙalin alƙalan Najeriya ba a London’



Tinubu

Zaɓabben shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya musanta rahotannin da ke cewa ya gana da babban jojin Najeriya a birnin London na ƙasar Ingila.

Wata sanarwa da ta samu sa hannun daraktan yaɗa labaru na kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Bayo Onanuga, ta bayyana labarin a matsayin ƙage maras tushe.

A cikin kwanakin nan ne wasu jaridu da kuma masu amfani da shafukan sada zumunta suka rinka yaɗa labarin yadda aka yi wata ganawar sirri, tsakanin Bola Ahmed Tinubu da babban jojin Najeriya, Olukayode Ariwoola.

Labarin ya nuna cewa babban jojin ya yi ɓadda-bami ta hanyar hawa keken guragu domin ganawa da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar a birnin London.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like