Tinubu zai jagoranci tawagar jiga-jigan jam’iyar APC zuwa Daura


Ana sa ran Bola Ahmad Tinubu, jagoran jam’iyar APC,zai jagoranci wata tawagar manyan ƴan jam’iyar zuwa Dauran jihar Katsina  inda za su gana da shugaban kasa Muhammad Buhari.

A cewar Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya jiga-jigan jam’iyar ta APC za su hallara a Daura domin yi wa shugaban ƙasar ta’aziyar mutane biyu da suka rasu a danginsa.

Tinubu da Bisi Akande sun gana da Buhari a ranar  13 ga watan Faburairu a fadar shugaban kasa dake Abuja.

A yayin ziyarar da suka kai masa Akande yace basun kai ziyarar bane dan tattauna batun siyasa ba, sun je ne domin yiwa shugaban gaisuwar ta’aziyar rashi da aka yi masa.

A cewar wata majiya ziyarar ta ranar Asabar ta wuce gaisuwar mutuwa kaɗai akwai batutuwa da dama da za su tattauna ciki har da batun sake tsayawa takarar shugaban a shekarar 2019.

A ranar juma’a ne shugaba Buhari ya karɓi baƙuncin gwamnonin jam’iyar APC a Daura.

You may also like